24 episodios

Wayar da kan jama’a da ilmantar da su, game da sha’anin da ya shafi Noma da muhalli da canjin yanayi. Yin bayanai dangane da batun gurbacewar yanayi tare da dumamarsa (Yanayi).

Muhallinka Rayuwarka RFI Hausa

    • Noticias

Wayar da kan jama’a da ilmantar da su, game da sha’anin da ya shafi Noma da muhalli da canjin yanayi. Yin bayanai dangane da batun gurbacewar yanayi tare da dumamarsa (Yanayi).

    Nigeria daya daga cikin kasashe masu noman auguda a nahiyar Afrika da duniya

    Nigeria daya daga cikin kasashe masu noman auguda a nahiyar Afrika da duniya

    Shirin a wannan mako zai ba da hankali ne akan noman auduga,

    a shekarun baya, Nigeria ta kasance daya daga cikin kasashe masu tinkaho da noman auguda a nahiyar Afrika da duniya baki daya.

    Sai dai hankalin mahukuntan kasar ya koma ga bangaren man petur bayanda Allah ya albarkaci kasar da mai.

    Jihohin da suka yi fice a noman auduga a kasar, sun hada da Zamfara, Katsina, Kano, Adamawa, Bauchi da kuma Gombe.

    • 17 min
    Matsalar yoyon iskar gas yayi sanadiyyar gurbacewar ruwan sha yankin Delta

    Matsalar yoyon iskar gas yayi sanadiyyar gurbacewar ruwan sha yankin Delta

    Shirin na wannan mako zai yi dubi ne akan  yadda al'ummar karamar hukumar Obagi na jihar RIVERS dake yankin NIGER DELTA tarayyar Najeriya suke fama da matsalar yoyon iskar gas sanadiyar fashewar bututun da aka samu tun a watan Yunin shekarar 2023  wanda yayi sanadiyyar gurbacewar ruwan sha, wanda ya sa al'ummar ke kamuwa da cutar amai da gudawa  har zuwa wannan lokaci.

    • 19 min
    Matakan da gwamnatin Najeriya ke dauka don magance matsalar tsuntsaye a gonaki

    Matakan da gwamnatin Najeriya ke dauka don magance matsalar tsuntsaye a gonaki

    Shirin 'Muhalli' na wannan makon tare da Nasiru Sani ya mayar da hankali ne kan tu’annatin da wasu nau'in tsuntsaye  da ake kira jan-baki ke yi wa gonaki a Najeriya tare da kokarin da gwamnati ke yi domin shawo kan lamarin.

    • 19 min
    Yadda tsananin zafi ya ci karo da lokacin azumin watan Ramadana

    Yadda tsananin zafi ya ci karo da lokacin azumin watan Ramadana

    Shirin a wannan mako zai ba da hankali ne akan tsananin zafin da ake fama da shi a wasu yankuna na Nahiyar Afirka,  a wannan shekarar ya tsananta inda a wasu sassa na tarayyar Najeriya lamarin ya dan wuce misali.

    Jihar Sokoto da ke Arewacin Najeriya, jiha ce da tun asali aka sani da tsanantar kowane juyin yanayi na Zafi ko na Sanyin Hunturu ko ma na yawan saukar Ruwan sama.

    Sai a latsa alamar sauti domin sauraron shirin.

    • 20 min
    Kaddamar da shirin inganta harkokin noma a jihar Niger

    Kaddamar da shirin inganta harkokin noma a jihar Niger

    Shirin na wanna makon zai yi dubi ne akan katafaren shirin zamanantar da aikin noma da gwamnatin jihar Nejan Najeriya ta kaddamar. Masana na ganin Jihar a matsayin wadda idan aka tattala kasar noma da take da ita, a cikinta kadai za a iya noma abincin da zai iya ciyar da kasar har ma a iya fitarwa zuwa kasashen ketare.

    • 20 min
    Najeriya ta kasance kan gaba a fagen noman masara a yankin yammacin Afrika

    Najeriya ta kasance kan gaba a fagen noman masara a yankin yammacin Afrika

    Shirin wannan mako zai ba da hankali ne a kan yadda Najeriya ta kasance akan gaba a fagen noman masara a daukacin yankin yammacin Afrika, inda kasar ke samar da sama da kashi 48 na masarar da ake nomawa a yankin.

    Mafi yawan masarar da ake nomawa a kasar, na fitowa ne daga yankin arewacin kasar, musamman jihohin Bauchi, Kaduna, Borno, Naija da Taraba da kuma wasu ‘yan kalilan din jihohin kudu maso yammacin kasar.

    • 21 min

Top podcasts de Noticias

Más de uno
OndaCero
Es la Mañana de Federico
esRadio
La Trinchera de Llamas
esRadio
La rosa de los vientos
OndaCero
Herrera en COPE
COPE
A vivir que son dos días
SER Podcast

Más de RFI Hausa

Tarihin Afrika
RFI Hausa
Tambaya da Amsa
RFI Hausa
Wasanni
RFI Hausa
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
RFI Hausa
Mu Zagaya Duniya
RFI Hausa
Lafiya Jari ce
RFI Hausa