Daga cikin labarun da shirin na Muzagaya Duniya ya sake waiwaya akwai cikar Sashin Hausa na RFI shekaru 17 cif da kafuwa. Sai kuma matakin rushe sabbin masarautun da ya baiwa gwmna Abba Kabir Yusuf damar sake naɗa Sarki Muhammadu Sunusi na II a matsayin Sarkin Kano na 16.
A Guinea kuwa, gwamnatin sojin da ke jagorantar ƙasar ce ta rufe wasu kafafen yaɗa labarai da suka hada da gidan talabijin da kuma gidajen radio da dama.
Kotun Duniya ta baiwa Isra’ila Umarnin Dakatar da hare-haren da ta kaiwa a Rafah.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.....
Informazioni
- Podcast
- FrequenzaOgni settimana
- Uscita25 maggio 2024 10:50 UTC
- Durata20 min
- ClassificazioneContenuti adatti a tutti