Dandalin Siyasa RFI Hausa
-
- Nachrichten
Shirin Dandalin Siyasa, yana tattaunawa tare da tafka muhawar kan al’amurran siyasa da ke faruwa a kasashen duniya, da batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, wanda Bashir Ibrahim Idris ke jagoranta. Wannan Shirin na zuwa ne a karshen mako Ranar Assabar da maimaci a ranar Lahadi a Shirye Shiryen Safe da Yamma.
-
Majalisar Najeriya ta gayyaci Buhari don yi mata bayani kan tsaro
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari kan kiran da Majalisar Tarayyar Najeriya ta yi shugaba Muhammadu Buhari don yi mata bayani kan tabarbarewar tsaro a kasar.
-
Rikicin shugabancin Majalisar Wakilai a Najeriya
Shirin dandalin siyasa a wannan makon ya sake yin duba kan dambarwar neman shugabancin Majalisar Najeriyar karo na 9 da sabbin zababbun 'yan Majalisar wakilan kasar ke tafkawa. A yi sauraro lafiya.
-
Dambarwar Jam'iyyar APC kan shugabancin Majalisun Najeriya
Har yanzu Jam'iyyar APC ta gaza shawo kan matsalolinta da suka shafi 'yan majalisun da za su jagoranci majalisar Dattijai da ta wakilai, dai dai lokacin da ake ci gaba da fuskantar rarrabuwar kai.
-
Fatan yan Najeriya dangane da sabuwar Majalisa bayan zabe
Bayan wata daya da kawo karshen zaben Shugaban kasa da na wasu yan majalisu a Najeriya,hankulan yan kasar da dama ya koma zuwa zauren Majalisa .
Haka zalika wasu daga cikin yan majalisun da suka samu goyan bayan jama'a sun sheidawa Bashir Ibrahin Idris a cikin shirin Siyasa fatan su da kuma irinn rawar da za su iya takawa a Majalisa don kawo sauyi a siyasar kasar,banda haka wasu sun bayyana damuwa a kai. -
Dambarwar zabukan Najeriya na 2019
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan dambarwar zabukan Najeriya, in da Jam'iyyar adawa ta PDP ta garzaya kotu domin kalubalantar nasarar shugaba Muhammadu Buhari na APC a zaben 2019, yayinda ita ma APC a jihar Bauchi ta ruga zuwa kotu duk dai akan batun na zabe.
-
Nazari kan zaben Gwamnoni a Najeriya
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari ne game da zabukan Gwamnoni na 'yan majalisun jihohin Najeriya da za a gudanar a ranar Asabar mai zuwa, in da ake fargabar cewa, da dama daga cikin Gwamnoni masu ci ba za su koma kan kujerunsu ba saboda wasu dalilai na siyasa.